Wasu sabbin kungiyoyin addinin musulunci sun fito a jihohin Arewa.
Wadannan Mutanen ma da kuke gani suna daura Qur'ani a kai suna yayin addu'a.
Indai da ranka kasha kallo a wannan duniyar, wadannan wasu mutane ne da suke taruwa a wani masalacci suyi sahu sahu suna karanta Alqur'ani yayin da suka dorashi bisa kawunansu.
Sai dai wannan sabuwar akidar ta janyo cece kuce a tsakanin al’umma Muslmi, yayinda wasu ke mamakin shin wannan wace irin kungiya ce, kuma shin wannan abu ya halasta, kuma wanene musababbin kawo wannan akidar?
Ya Allah ka doramu bisa hanya mai kyau...